Home General Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano ta ce za ta fito da wasu da Sabbin hanyoyin tattara zakkah tare Kuma da rabawa mabukata yadda yakamata

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka Lokacin kaddamar da shugabannin hukumomi biyu na Shari’a da na Zakkah a gidan Gwamnati.

Abba Kabir Yusuf ya ce Jihar Kano na da dimbin attajirai, to sai dai a bangare guda ta na fama da yawan almajirai da mabarata , Wanda ya bukaci hukumar Zakkah da KHubsi da ta fito da wasu hanyoyi na karba Zakkah daga wajen attajirai a wani yunkuri na rage yawan mabarata a JIhar kano.

Shugabannin hukumomin da Gwamnan ya kaddamar sun hada da Barrister Habibu Shekh Dan Almajiri a matsayin Shugaban hukumar Zakkah da Khubsi, sai Shekh Abbas Abubakar Daneji a matsayin Shugaban hukumar Shari’a.

Sauran wakilan hukumar sun hada da Shekh Malam Ali Dan Abba a matsayin kwamishina na biyu a hukumar shari’ah da Malam Abubakar madatai Mai Ashafa da sayyadi Nafi’u Umar Harazumi da Kuma alaramma Gwani Hadi Gwani Tahir

Wakilinmu na fadar Gwamnati ya ruwaito mana Gwamnan na Jan hankulan malaman da su yi amfani da gogewa da Ilimi wajen fito da Sabbin tsare tsare da za su kawo ci gaban addinin musulunci a Jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp