Home General Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano ta ce za ta fito da wasu da Sabbin hanyoyin tattara zakkah tare Kuma da rabawa mabukata yadda yakamata

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka Lokacin kaddamar da shugabannin hukumomi biyu na Shari’a da na Zakkah a gidan Gwamnati.

Abba Kabir Yusuf ya ce Jihar Kano na da dimbin attajirai, to sai dai a bangare guda ta na fama da yawan almajirai da mabarata , Wanda ya bukaci hukumar Zakkah da KHubsi da ta fito da wasu hanyoyi na karba Zakkah daga wajen attajirai a wani yunkuri na rage yawan mabarata a JIhar kano.

Shugabannin hukumomin da Gwamnan ya kaddamar sun hada da Barrister Habibu Shekh Dan Almajiri a matsayin Shugaban hukumar Zakkah da Khubsi, sai Shekh Abbas Abubakar Daneji a matsayin Shugaban hukumar Shari’a.

Sauran wakilan hukumar sun hada da Shekh Malam Ali Dan Abba a matsayin kwamishina na biyu a hukumar shari’ah da Malam Abubakar madatai Mai Ashafa da sayyadi Nafi’u Umar Harazumi da Kuma alaramma Gwani Hadi Gwani Tahir

Wakilinmu na fadar Gwamnati ya ruwaito mana Gwamnan na Jan hankulan malaman da su yi amfani da gogewa da Ilimi wajen fito da Sabbin tsare tsare da za su kawo ci gaban addinin musulunci a Jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp