Home General Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano za ta fito da wasu hanyoyin tattara zakkah

Gwamnatin Kano ta ce za ta fito da wasu da Sabbin hanyoyin tattara zakkah tare Kuma da rabawa mabukata yadda yakamata

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka Lokacin kaddamar da shugabannin hukumomi biyu na Shari’a da na Zakkah a gidan Gwamnati.

Abba Kabir Yusuf ya ce Jihar Kano na da dimbin attajirai, to sai dai a bangare guda ta na fama da yawan almajirai da mabarata , Wanda ya bukaci hukumar Zakkah da KHubsi da ta fito da wasu hanyoyi na karba Zakkah daga wajen attajirai a wani yunkuri na rage yawan mabarata a JIhar kano.

Shugabannin hukumomin da Gwamnan ya kaddamar sun hada da Barrister Habibu Shekh Dan Almajiri a matsayin Shugaban hukumar Zakkah da Khubsi, sai Shekh Abbas Abubakar Daneji a matsayin Shugaban hukumar Shari’a.

Sauran wakilan hukumar sun hada da Shekh Malam Ali Dan Abba a matsayin kwamishina na biyu a hukumar shari’ah da Malam Abubakar madatai Mai Ashafa da sayyadi Nafi’u Umar Harazumi da Kuma alaramma Gwani Hadi Gwani Tahir

Wakilinmu na fadar Gwamnati ya ruwaito mana Gwamnan na Jan hankulan malaman da su yi amfani da gogewa da Ilimi wajen fito da Sabbin tsare tsare da za su kawo ci gaban addinin musulunci a Jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp