NLC ta dakatar da yin zanga-zanga Kan tsadar Data da kudin kira

Kungiyar kwadago ta janye zanga Zangar da ta shirya gudanar wa a Talatar nan sakamakon Karin kudin kiran waya da na Data.

Wannan ya biyo bayan wata ganawa da ta yi da wakilan gwamnati a ofishin sakataren gwamnatin tarayya a daren Litinin, kungiyar kwadagon ta ce ta yanke shawarar dakatar da zanga-zangar har sai an dawo teburin tattaunawa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, shugaban kungiyar na kasa Joe Ajaero, ya ce gwamnati ta amince da kafa wani babban kwamiti da zai duba daukacin tsarin kudin Kiran waya.

A cewarsa, kwamitin zai kunshi wakilai biyar daga bangarorin biyu kuma ana sa ran zai mika rahoton bincikensa cikin makonni biyu.

Ya kara da cewa kungiyar za ta dauki matakan zanga-zanga da yajin aiki nan gaba, mutukar ba’a Sami wata matsaya ba kan rahoton Kwamitin .

Idan za,a iya tunawa dai a makonnin da Suka gabata ne hukumar Sadarwa ta kasa ta amincewa kamfanonin sadarwa masu zaman kanau da su kara kashi Hamsin na kudin Kiran waya da na amfani da data, wacce ta Kai ga kungiyar kwadago barazanar fita zanga zanga a ranar hudu ga watan Fabarairu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 12 hours 12 minutes 39 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 13 hours 54 minutes 4 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com