Dakarun Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 82 tare da kama 198 a mako guda

Shelkwatar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun kashe ƴan ta’adda 82  tare da kama guda 198, suka kuma ceto mutane 93 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda da ya wuce a sassan ƙasar.

Daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar, Manjo Janar Markus Kangye,  ne ya bayyana haka a Abuja,  a yayin da ya ke yi wa manema labarai bitar nasarorin  da dakarun ƙasar suka samu.

Kangye  yace dakarun sun kuma ƙwace ɗimbim makamai da ababen hawa a daga ƴan ta’addan a samamen da suka yi daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Fabrairu.

Ya ce dakarun sun ƙwace bindigogi da suka haɗa da AK47 guda 46, bindigogin da aka ƙera a gida guda 18, sai bindigogin zari-ruga guda 19 da harshasai sama 1,200.

Kakakin ma’aikatar tsaron ya ƙara da cewa ƴan ta’addda 41 sun miƙa wuya ga dakarun rundunar Operation HADIN KAI a yankin arewa maso gabashin ƙasar, kuma daga cikin su akwai manya baligai 41, sai yara 19.

Janar Kangye ya ƙara da cewa dakarun na Najeriya sun kama masu satar mai a yankin Kudu maso Kudancin ƙasar, sun kuma daƙile satar da kiyasta darajarta ta kai naira 587.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 2 hours 26 minutes 59 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 4 hours 8 minutes 24 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com