Shelkwatar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun kashe ƴan ta’adda 82 tare da kama guda 198, suka kuma ceto mutane 93 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda da ya wuce a sassan ƙasar.
Daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya bayyana haka a Abuja, a yayin da ya ke yi wa manema labarai bitar nasarorin da dakarun ƙasar suka samu.
Read Also:
Kangye yace dakarun sun kuma ƙwace ɗimbim makamai da ababen hawa a daga ƴan ta’addan a samamen da suka yi daga ranar 14 zuwa 21 ga watan Fabrairu.
Ya ce dakarun sun ƙwace bindigogi da suka haɗa da AK47 guda 46, bindigogin da aka ƙera a gida guda 18, sai bindigogin zari-ruga guda 19 da harshasai sama 1,200.
Kakakin ma’aikatar tsaron ya ƙara da cewa ƴan ta’addda 41 sun miƙa wuya ga dakarun rundunar Operation HADIN KAI a yankin arewa maso gabashin ƙasar, kuma daga cikin su akwai manya baligai 41, sai yara 19.
Janar Kangye ya ƙara da cewa dakarun na Najeriya sun kama masu satar mai a yankin Kudu maso Kudancin ƙasar, sun kuma daƙile satar da kiyasta darajarta ta kai naira 587.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 2 hours 26 minutes 59 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 4 hours 8 minutes 24 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com