Home General Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Akpabio da Natasha: Ku yi hankali kada kimar majalisa ta zube- Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki ya yi kira ga dukkan ɓangarorin shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti da su iya bakinsu domin kare martabar majalisar.

A baya-bayan nan dai shugaban Majalisar Dattawan Sanata Godswill Akpabio ya riƙa samun saɓani da Sanata Natasha, lamarin da ya sa har Natasha ta shigar da shi ƙara a gaban kotu, kan zargin ɓata mata suna.

To sai dai tsohon Shugaban Majalisar Sanata Saraki ya ja kunne duka ɓangarorin don kauce wa zubar wa majalisar kima.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Saraki ya ce abin da ya farun bai kamata ba, “wannan ya sa nake ganin ɓangarorin biyu da magoya bayansu na cikin majalisa da wajenta kowa ya iya bakinsa, kowa ya san tasirin da abin da yake aikatawa ko ya faɗa zai iya yi ga majalisar domin kare daraja da ƙimar da majalisa take da ita.”

Ya ce ya zama dole a bi dokar kundin tsarin mulki da dokokin majalisa wajen kawo ƙarshen wannan taƙaddama da ke tsakanin mutanen biyu.

“Sannan a yi komai a buɗe, ba tare da ba wa wani ɓangare fifiko ba. Abin da ya kamata a saka a gaba shi ne fito da gaskiya da kuma kare mutuncin majalisa wadda ita ce take da alhakin yin doka a ƙasa, saboda haka tana buƙatar a yi ƙoƙarin ba ta kariya da fito da mutuncinta.”

Ya ce a lokacin da yake shugaban majalisar, wani sanata ya zarge shi da fasaƙwaurin mota, “wanda hakan ya sa aka kafa kwamiti kuma a gaban ƴan jarida na kare kaina a gaban kwamitin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp