Home General An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

Shugaban ƙaramar hukumar Okehi da ke jihar Kogi, Amoka Monday, ya ayyana dokar taƙaita zirga-zirga a yankin ƙaramar hukumar sakamakon fargabar ɓarkewar rikici saboda haramta tarukan siyasa da gwamnan jihar ya yi a ranar Litinin.

A watan sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar ya sanya wa hannu wadda jaridar Punch ta rawaito, Amoka Monday ya ce dokar taƙaita zirga-zirgar dole ce domin samar da zaman lafiya a ƙaramar hukumar.

Wannan dai ya biyo bayan sanarwar da Sanata Natasha ta fitar tana mai nanata cewa za ta yi gangamin siyasa a ƙaramar hukumar duk da hanin da rundunar ƴansandan jihar ta yi mata.

A ranar Litinin ne gwamna Ododo ya haramta dukkan wani taron siyasa a jihar.

Magoya bayan Sanata Natasha dai sun ce za su yi wannan gangami ne domin nuna goyon baya ga wakiliyar tasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp