An saka dokar taƙaice zirga-zirga a mazaɓar Sanata Natasha

Shugaban ƙaramar hukumar Okehi da ke jihar Kogi, Amoka Monday, ya ayyana dokar taƙaita zirga-zirga a yankin ƙaramar hukumar sakamakon fargabar ɓarkewar rikici saboda haramta tarukan siyasa da gwamnan jihar ya yi a ranar Litinin.

A watan sanarwa da shugaban ƙaramar hukumar ya sanya wa hannu wadda jaridar Punch ta rawaito, Amoka Monday ya ce dokar taƙaita zirga-zirgar dole ce domin samar da zaman lafiya a ƙaramar hukumar.

Wannan dai ya biyo bayan sanarwar da Sanata Natasha ta fitar tana mai nanata cewa za ta yi gangamin siyasa a ƙaramar hukumar duk da hanin da rundunar ƴansandan jihar ta yi mata.

A ranar Litinin ne gwamna Ododo ya haramta dukkan wani taron siyasa a jihar.

Magoya bayan Sanata Natasha dai sun ce za su yi wannan gangami ne domin nuna goyon baya ga wakiliyar tasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com