Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Shamsedeen Babatunde Ogunjimi, a matsayin sabon Akanta Janar na ƙasar.
Mashawarcin shugaban ƙasar kan yaɗa labarai da tsare-tsare, Boyo Onanuga ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu, inda ya ce shugaban ya naɗa shi ne bayan an tantance shi.
Nadin nasa, wanda aka amince da shi a yau, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da wanda yake kan mukamin Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.
Read Also:
Sanarwar ta ce sai da shugaba Tinubu ya sa aka bi matakai daban-daban, wajen tantance Ogunjimi mai shekaru 57 domin tabbatar da ƙwarewarsa.
Ogunjimi ya kammala karatunsa na digirin farko a Jami’ar Nsukka, a shekarar 1990, inda ya karanci harkar akanta, sannan kuma ya sami digiri na biyu a fannin tsumi (Accounting) a Jami’ar Legas, a inda yanzu haka Mamba ne a Cibiyar Akantoci ta Najeriya.
A ƙarshe Tinubu ya buƙace shi da ya dage wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa Najeriya hidima cikin gaskiya, ƙwarewa, da sadaukarwa ga hidimar ƙasar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 16 hours 50 minutes 19 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 18 hours 31 minutes 44 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com