Home General Tinubu ya nada sabon Akanta Janar a Nijeriya

Tinubu ya nada sabon Akanta Janar a Nijeriya

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Shamsedeen Babatunde Ogunjimi, a matsayin sabon Akanta Janar na ƙasar.

Mashawarcin shugaban ƙasar kan yaɗa labarai da tsare-tsare, Boyo Onanuga ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu, inda ya ce shugaban ya naɗa shi ne bayan an tantance shi.

Nadin nasa, wanda aka amince da shi a yau, zai fara aiki ne daga ranar 7 ga Maris 2025, ranar da wanda yake kan mukamin Oluwatoyin Madehin zai yi ritaya.

Sanarwar ta ce sai da shugaba Tinubu ya sa aka bi matakai daban-daban, wajen tantance Ogunjimi mai shekaru 57 domin tabbatar da ƙwarewarsa.

Ogunjimi ya kammala karatunsa na digirin farko a Jami’ar Nsukka, a shekarar 1990, inda ya karanci harkar akanta, sannan kuma ya sami digiri na biyu a fannin tsumi (Accounting) a Jami’ar Legas, a inda yanzu haka Mamba ne a Cibiyar Akantoci ta Najeriya.

A ƙarshe Tinubu ya buƙace shi da ya dage wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa Najeriya hidima cikin gaskiya, ƙwarewa, da sadaukarwa ga hidimar ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp