Home General Tinubu ya bawa Jega Mukami

Tinubu ya bawa Jega Mukami

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya nada Farfesa Attahiru Jega a matsayin mai ba shi shawara kuma babban jami’in kwamitin bunkasa kiwon dabbobi na kasar.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Attahiru Jega mai shekaru 68 ya rike mukamin shugaban hukumar zaben Nijeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015.

Kafin mukamin da Shugaba Tinubu ya ba shi a yammacin Jumma’ar nan, shi ne ya jagoranci kwamitin gyaran kiwon dabbobi da ya bai wa gwamnatin Tinubu shawarar kafa ma’aikata ta musamman don bunkasa kiwon dabbobi wacce yanzu ke da minista.

Sanarwar ta ce ana sa rana Farfesa Attahiru Jega zai yi amfani da gogewar da wajen habbaka harkokin kiwon dabbobi a Nigeria kamar yadda suka bayar da samar da ma’aikata sukutum da guda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp