Hukumar Kula da Albarkatun Mai Na Ƙasa (NMDPRA) ta bayar da lasisin buɗe sabbin matatun man fetur a Najeriya.
Hukumar ta ce ta ba wasu kamfanoni guda uku lasisin ne domin buɗe matatun a jihohin Abia da Delta da Edo.
Read Also:
Shafin intanet na tashar Channels ne ya kalato labarin daga shafin X na NMDPRA, inda ya ƙara da cewa za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a jihar Edo.
Za kuma da Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a jihar Abia, kamar yadda sanarwar, wadda shugaban hukumar, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.
Idan aka kammala su, matatun guda uku za su riƙa tace ganga 140,000 ke nan a kullum.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1486 days 21 hours 50 minutes 58 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1468 days 23 hours 32 minutes 23 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com