PDP ta sake ɗage babban Taron ta na NEC

Babbar jam’iyyar a Najeriya wato PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa wato taron NEC, wanda yanzu aka mayar ranar 15 ga Mayun 2025.

Jam’iyyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, wadda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye ya sanya wa hannu.

Asali jam’iyyar ta sanar za ta yi babban taron ne a ranar 13 ga Maris, sannan aka ɗage saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka yi a wasu jihohi da yankuna.

Tun a shekarar da ta gabata ce dai aka saka ranar babban taron na 98, amma ana ɗagewa, wanda wataƙila hakan bai rasa nasaba da wasu matsaloli da jam’iyyar ke fuskanta.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 16 minutes 8 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 1 hour 57 minutes 33 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com