Home General PDP ta sake ɗage babban Taron ta na NEC

PDP ta sake ɗage babban Taron ta na NEC

Babbar jam’iyyar a Najeriya wato PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa wato taron NEC, wanda yanzu aka mayar ranar 15 ga Mayun 2025.

Jam’iyyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, wadda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye ya sanya wa hannu.

Asali jam’iyyar ta sanar za ta yi babban taron ne a ranar 13 ga Maris, sannan aka ɗage saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka yi a wasu jihohi da yankuna.

Tun a shekarar da ta gabata ce dai aka saka ranar babban taron na 98, amma ana ɗagewa, wanda wataƙila hakan bai rasa nasaba da wasu matsaloli da jam’iyyar ke fuskanta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp