Duk abin da zan yi sai na tuntubi Buhari – Nasir El-Rufai

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya ce bai bar jam’iyya mai mulki ta APC ba har sai da tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya amince da batun barinsa jam’iyyar APC da komawa jam’iyyar SDP.

“Da saninsa na bar APC. Sai da na je ranar Juma’a na faɗa masa cewa zan bar jam’iyyar. Saboda babu wani abun da nake yi ba tare da na sanar da shi ba.

Sashen Hausa na bbc ya wallafa El-Rufai na cewa “Ko lokacin da nake gwamnan Kaduna da zan naɗa kwamishoni sai da na kai masa jerin sunayen domin ya duba ya gani ko a ciki akwai wanda ya taɓa zagin sa”.

Bayan ya duba ya ce ba matsala Allah ya yi albarka. Duk abin da zan yi sai na yi shawara da shi.” In ji Malam El-Rufai.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 15 hours 1 minute 25 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 42 minutes 50 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com