Inganta rayuwar AL’umma ce a gabana ba zaben 2027

Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu ya mayar da hankali ne ga kyautata rayuwar ƴan ƙasar, amma ba wai ga zaɓen 2027 ba.

Mai taimaka wa shugaban kan harkokin sadarwa, Sunday Dare wanda ya bayyana haka a shafin X ranar Juma’a, ya ce za a ga nasarorin da gwamnatin Tinubu ta cimma zuwa karshen wa’adinsa na mulki, ta yadda ya kawo ci gaba ga ɓangaren tattali arzikin ƙasar.

Sanarwar ta Mista Dare na zuwa ne a daidai lokacin da turka-turkar siyasa da kuma tsadar rayuwa ke ƙaruwa a ƙasar.

“Tinubu bai damu da babban zaɓen Najeriya na gaba ba. Ya damu ne kawai kan irin ci gaban da zai kawowa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa shugaban ya kuma damu kan yadda tsare-tsaren da ya kawo za su haifar da ɗa mai ido.

“Mun ga saukar hauhawar farashi, mun ga kyautatuwar hada-hadar kasuwanni da kuma harkokin shige da fice na kayayyaki,” in ji sanarwar.

Ta kuma ce an samu zuba-jari da ya kai naira biliyan 50, har ma da saukar farashin kayayyaki.

Sai dai ƴan Najeriya na ci gaba da ƙoƙawa dangane da tsadar rayuwa da suka ce manufofin shugaban sun jefa su, musamman ma cire tallafin man fetur da ya yi lokacin rantsuwar kama aiki.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 53 minutes 55 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 35 minutes 20 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com