Home General Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi...

Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi safararsa a Taraba

Hukumar hana fasa kwauri a Najeriya ta ce jami’anta na Operation Whirlwind sun ƙwace litar man fetur 34,470 wanda aka yi safararsa a jihar Taraba, a ƙoƙari da take yi wajen yaƙi da masu safarar mai

Babban Kwanturola na hukumar ta kwastam, Bashir Adewale ne ya sanar da haka ga manema labarai a Jalingo, inda ya ce sun samu nasarar ce a garin Gembu na karamar hukumar Sardauna a jihar da kuma Kan-Iyaka da ke makwabtaka da ƙasar Kamaru.

Hanyar da ta bi Kan-Iyakar dai ta kasance gungun wuri da aka fi safarar man fetur zuwa waje.

Adewale ya ce sun kuma ƙwace wata babbar mota dakon kaya da aka yi amfani da ita wajen safarar mai ɗin, inda ya ƙara da cewa sun kai samamen ne tare da haɗin gwiwar hukumar kula da sarrafawa da kuma tace man fetur (NMDPRA) da kuma taimakon ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

“Mun ƙwato jarakuna mai 1,149 – kowane yana ɗauke da lita 30, abin da ya tashi zuwa lita 34,470,” in ji Adewale.

Ya ce masu safarar barazana ne ga tsaron ƙasar kuma ya zama wajibi a kama tare da hukunta su.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su bai wa gwamnati haɗin-kai domin tabbatar da ganin cewa an kakkaɓe ɓata-garin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp