Home General Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi...

Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi safararsa a Taraba

Hukumar hana fasa kwauri a Najeriya ta ce jami’anta na Operation Whirlwind sun ƙwace litar man fetur 34,470 wanda aka yi safararsa a jihar Taraba, a ƙoƙari da take yi wajen yaƙi da masu safarar mai

Babban Kwanturola na hukumar ta kwastam, Bashir Adewale ne ya sanar da haka ga manema labarai a Jalingo, inda ya ce sun samu nasarar ce a garin Gembu na karamar hukumar Sardauna a jihar da kuma Kan-Iyaka da ke makwabtaka da ƙasar Kamaru.

Hanyar da ta bi Kan-Iyakar dai ta kasance gungun wuri da aka fi safarar man fetur zuwa waje.

Adewale ya ce sun kuma ƙwace wata babbar mota dakon kaya da aka yi amfani da ita wajen safarar mai ɗin, inda ya ƙara da cewa sun kai samamen ne tare da haɗin gwiwar hukumar kula da sarrafawa da kuma tace man fetur (NMDPRA) da kuma taimakon ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

“Mun ƙwato jarakuna mai 1,149 – kowane yana ɗauke da lita 30, abin da ya tashi zuwa lita 34,470,” in ji Adewale.

Ya ce masu safarar barazana ne ga tsaron ƙasar kuma ya zama wajibi a kama tare da hukunta su.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su bai wa gwamnati haɗin-kai domin tabbatar da ganin cewa an kakkaɓe ɓata-garin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp