Home General Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi...

Kwastam ta ƙwace sama da lita 34,000 na fetur da aka yi safararsa a Taraba

Hukumar hana fasa kwauri a Najeriya ta ce jami’anta na Operation Whirlwind sun ƙwace litar man fetur 34,470 wanda aka yi safararsa a jihar Taraba, a ƙoƙari da take yi wajen yaƙi da masu safarar mai

Babban Kwanturola na hukumar ta kwastam, Bashir Adewale ne ya sanar da haka ga manema labarai a Jalingo, inda ya ce sun samu nasarar ce a garin Gembu na karamar hukumar Sardauna a jihar da kuma Kan-Iyaka da ke makwabtaka da ƙasar Kamaru.

Hanyar da ta bi Kan-Iyakar dai ta kasance gungun wuri da aka fi safarar man fetur zuwa waje.

Adewale ya ce sun kuma ƙwace wata babbar mota dakon kaya da aka yi amfani da ita wajen safarar mai ɗin, inda ya ƙara da cewa sun kai samamen ne tare da haɗin gwiwar hukumar kula da sarrafawa da kuma tace man fetur (NMDPRA) da kuma taimakon ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

“Mun ƙwato jarakuna mai 1,149 – kowane yana ɗauke da lita 30, abin da ya tashi zuwa lita 34,470,” in ji Adewale.

Ya ce masu safarar barazana ne ga tsaron ƙasar kuma ya zama wajibi a kama tare da hukunta su.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su bai wa gwamnati haɗin-kai domin tabbatar da ganin cewa an kakkaɓe ɓata-garin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp