Home General Inganta rayuwar AL’umma ce a gabana ba zaben 2027

Inganta rayuwar AL’umma ce a gabana ba zaben 2027

Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu ya mayar da hankali ne ga kyautata rayuwar ƴan ƙasar, amma ba wai ga zaɓen 2027 ba.

Mai taimaka wa shugaban kan harkokin sadarwa, Sunday Dare wanda ya bayyana haka a shafin X ranar Juma’a, ya ce za a ga nasarorin da gwamnatin Tinubu ta cimma zuwa karshen wa’adinsa na mulki, ta yadda ya kawo ci gaba ga ɓangaren tattali arzikin ƙasar.

Sanarwar ta Mista Dare na zuwa ne a daidai lokacin da turka-turkar siyasa da kuma tsadar rayuwa ke ƙaruwa a ƙasar.

“Tinubu bai damu da babban zaɓen Najeriya na gaba ba. Ya damu ne kawai kan irin ci gaban da zai kawowa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa shugaban ya kuma damu kan yadda tsare-tsaren da ya kawo za su haifar da ɗa mai ido.

“Mun ga saukar hauhawar farashi, mun ga kyautatuwar hada-hadar kasuwanni da kuma harkokin shige da fice na kayayyaki,” in ji sanarwar.

Ta kuma ce an samu zuba-jari da ya kai naira biliyan 50, har ma da saukar farashin kayayyaki.

Sai dai ƴan Najeriya na ci gaba da ƙoƙawa dangane da tsadar rayuwa da suka ce manufofin shugaban sun jefa su, musamman ma cire tallafin man fetur da ya yi lokacin rantsuwar kama aiki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp