Home General Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro a jihar Katsina sun samu nasarar daƙile yunƙurin ƴanbindiga na kai hari a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jiyar, wadda take arewa maso yammacin ƙasar.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce jami’an tsaron sun samu nasarar ne a ranar Asabar.

“A ranar 15 ga watan Maris ce jami’an tsaron farin kaya suka samu bayanan sirri cewa ƴanbindiga suna taruwa a tsaunin Maijele da ke ƙaramar hukumar Ɗanmusa domin kai hari a ƙauyen Ɗan Takuri.

“Da samun labarin ne jami’an tsaron haɗin gwiwa na ƴansanda da askawaran Katsina suka kai ɗauki, inda aka yi musayar wuta tsakanin ƴanbindigar da jami’an tsaro.”

Ya ce a ƙarshe dai jami’an tsaron sun samu nasarar fatattakar ƴanbindigar, tare da kashe ɗaya daga cikinsu, sannan aka ƙwato wasu makamai da ƙwayoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp