Home General Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro a jihar Katsina sun samu nasarar daƙile yunƙurin ƴanbindiga na kai hari a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jiyar, wadda take arewa maso yammacin ƙasar.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce jami’an tsaron sun samu nasarar ne a ranar Asabar.

“A ranar 15 ga watan Maris ce jami’an tsaron farin kaya suka samu bayanan sirri cewa ƴanbindiga suna taruwa a tsaunin Maijele da ke ƙaramar hukumar Ɗanmusa domin kai hari a ƙauyen Ɗan Takuri.

“Da samun labarin ne jami’an tsaron haɗin gwiwa na ƴansanda da askawaran Katsina suka kai ɗauki, inda aka yi musayar wuta tsakanin ƴanbindigar da jami’an tsaro.”

Ya ce a ƙarshe dai jami’an tsaron sun samu nasarar fatattakar ƴanbindigar, tare da kashe ɗaya daga cikinsu, sannan aka ƙwato wasu makamai da ƙwayoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp