Home General Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro sun dakile haring ‘yan bindiga a Jihar Katsina

Jami’an tsaro a jihar Katsina sun samu nasarar daƙile yunƙurin ƴanbindiga na kai hari a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jiyar, wadda take arewa maso yammacin ƙasar.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce jami’an tsaron sun samu nasarar ne a ranar Asabar.

“A ranar 15 ga watan Maris ce jami’an tsaron farin kaya suka samu bayanan sirri cewa ƴanbindiga suna taruwa a tsaunin Maijele da ke ƙaramar hukumar Ɗanmusa domin kai hari a ƙauyen Ɗan Takuri.

“Da samun labarin ne jami’an tsaron haɗin gwiwa na ƴansanda da askawaran Katsina suka kai ɗauki, inda aka yi musayar wuta tsakanin ƴanbindigar da jami’an tsaro.”

Ya ce a ƙarshe dai jami’an tsaron sun samu nasarar fatattakar ƴanbindigar, tare da kashe ɗaya daga cikinsu, sannan aka ƙwato wasu makamai da ƙwayoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp