Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunubu Ya sanya Dokar Ta baci a jihar Ribas sakamakon Rikici da yaki ci yaki cinyewa.
Bola ahmad Tunubu wanda yayi wani gajeren jawabi da Yammacin wanann rana a fadar Shugaban kasa, Yace abinda ke faruwa a jihar Ribas ba zai yiwu su bari ya cigaba da faruwa ba.
Saboda an gaza samun daidaito tsakanin gwamnan jihar Fubara da Majalisar Dokokin jihar tun bayan da kotun Koli ta yanke Hukunci.
Bola ahmad Tunubu ya kara da cewa Gwamnan jihar ya dauki matakin rushe Zauren majalisar kuma ya gaza gyarawa, wanda hakan yasa Yan majalisar Jihar suka gaza samun cikakken matsuguni da zasuyi aikinsu kamar yadda kundin tsarin Mulkin kasar nan ya tanadar.
Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas
Read Also:
Tinubu yace ya samu rahotanni dake nuna Yadda Yan bindiga suka fara kai hare hare manyan bututun Manfetur wanda hakan barazana ne.
Kuma Gwamnan jihar Da Mataimakinsa basu zo sun sanar dani yanayin tsaro dake fuskantar Jihar ba, don haka a matsayina na Shugaban kasa wajibi nayi amfani da dokar kasa da ta bani dama wajen kare rayuka da dukiyoyin alumma wajen sanya dokar tabaci a jihar.
Ina sanar da Yan Nijeriya cewa daga yau na dakatar da Gwamnan jihar ribas da Mataimakinsa da kuma dukkan Yan Majalisar jihar har na tsawon watanni 6.
Shugaban kasa bola Ahmad Tunubu ya sanar da Vice admiral Ibokette Ibas Mai ritaya a matsayin wanda zai kula da Tafiyar da jihar Ta Ribas
Sai dai kuma bangaren Sharia na jihar zai cigaba da tafiyar da aikinsa kamar Yadda suka saba acewar Shugaban kasa Bola Ahmad Tunubu.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 45 minutes 47 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 27 minutes 12 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com