Home General Kotu ta ɗage shari’ar Nnamdi Kanu bayan cigaba da zama a yau...

Kotu ta ɗage shari’ar Nnamdi Kanu bayan cigaba da zama a yau Juma’a

Jagoran haramtacciyar ƙungiyar ‘yan’aware ta Indigenous People of Biafra (IPOB) ya sake bayyana a gaban babbar kotun tarayya yau Juma’a a Abuja babban birnin Najeriya.

Sai dai ɗaya daga cikin lauyoyinsa Aloy Ejimakor ya ce kotun ƙarƙashin Mai Shari’a James Kolawole ta ɗage cigaba da sauraron ƙarar zuwa 29 ga watan Afrilu da kuma 2 da 6 ga watan Mayu na 2025.

Ci gaba da shari’ar ta Nnamdi Kanu na zuwa ne bayan Alƙaliyar Alƙalai Kudirat Kekere-Ekunnyefere ta saka Mai Shari’a James Kolawole Omotoshi a matsayin sabon alƙalin da zai saurari shari’ar bayan Kanu ya yi ƙorafi kan Mai Shari’a Binta Nyako.

An yi hasashen za a yi bitar tuhuma bakwai da gwamatin Najeriya ke yi wa Kanu yayin ci gaba da shari’ar, waɗanda suka jiɓanci tayar da fitina da kuma ta’addanci.

A watan Disamban 2023 ne Kotun Ƙoli ta umarci Kanu ya koma babbar kotun ta tarayya domin kare tuhumar da ake yi masa bayan Binta Nyako ta yi watsi da takwas cikin 15 da gwamnati ta gabatar a 2021.

Gwamnatin Najeriya ta kai Kanu kotu ne bayan kama shi a wata ƙasar waje a 2021, kuma har yanzu mambobin ƙungiyarsa da gwamnati ta haramta na ci gaba da neman ɓallewa daga Najeiriya domin kafa ƙasar Biafra.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp