Home General Bani da alaƙa da masu fasa bututun Mai – Fubara

Bani da alaƙa da masu fasa bututun Mai – Fubara

Gwamnan jihar Rivers da aka dakatar, Siminalaya Fubara ya musanta zargin da ake yaɗawa cewa yana da alaƙa da ƙungiyoyin ƴanbindiga da ke fasa bututun mai, inda ya ce hotuna da bidiyo da ake yaɗawa ƙarya ne.

Fubara ya bayyana haka ne a wata sanarwa da sakataren watsa labaransa, Nelson Chukwudi ya fitar, inda ya ce Fubara na alla-wadai da yada labaran na farfaganda.

Ya ce ana yaɗa labaran na ƙaryar ne domin a tayar da zaune tsaye a jihar, sannan a ɓata masa suna,

“Gwamna Fubara ba shi da wata alaƙa da ƙungiyoyin ƴanbindiga masu fasa bututun mai, kuma bai taɓa tunanin ƙulla wata alaƙa da su ba, sannan kuma ba zai taɓa alaƙa da ɓatagari da suke barazana ga zaman lafiya da tattalin arzikin jihar Rivers ba,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Fubara ya nanata shirinsa na tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa, inda ya ƙara da cewa ba a cin moriyar gwamnati ba tare da zaman lafiya ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp