Home General Demukradiyya ta Gaza yin Amfani a Afirka

Demukradiyya ta Gaza yin Amfani a Afirka

Tsoshon shugaban Najeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin demokradiyya ya gaza wajen kawo ci gaba a nahiyar Afrika.

Ya ce tsarin ya gaza ne saboda abin da ya ƙunsa bai zo daidai da al’adu, da yadda ake tafiyar da rayuwa a nahiyar ba, da abubuwan da mutanen nahiyar suka yi amanna da su ba.

Obasanjo ya bayyana hakan ne a Abuja, babban birnin Najeriya, a wurin wani taron bikin cika shekaru 60 a duniya na tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilan ƙasar, Emeka Ihedioha.

Tsohon shugaban ya yi nuni da cewa idan aka kalli yadda tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln, ya bayyana tsarin dimokuradiyya da cewa gwamnati ce ta mutane da mutane ke jagoranta domin al’umma.

Inda ya ƙara da cewa tsari ne da ake domin kowa ya amfana, ba wai wani bangare na al’umma ba ko wasu mutane ƙalilan ba.

Obasanjo ya kuma bayyana cewa kafin zuwan dimokuradiyyar ƙasashen yamma, Afrika na da nata tsarin shugabancin wanda ke kula da buƙatun kowa.

A cewarsa wannan tsarin shi ne dimokuradiyya, ba abin da ake kira dimokuradiyya ba a yau wanda ke bai wa shugabanni damar karɓar duk abin da suke so ba bisa ƙa’ida ba da kuma ta hanyar cin hanci da rashawa su ce wa mutane su je kotu idan suna da ja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp