Home General Demukradiyya ta Gaza yin Amfani a Afirka

Demukradiyya ta Gaza yin Amfani a Afirka

Tsoshon shugaban Najeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin demokradiyya ya gaza wajen kawo ci gaba a nahiyar Afrika.

Ya ce tsarin ya gaza ne saboda abin da ya ƙunsa bai zo daidai da al’adu, da yadda ake tafiyar da rayuwa a nahiyar ba, da abubuwan da mutanen nahiyar suka yi amanna da su ba.

Obasanjo ya bayyana hakan ne a Abuja, babban birnin Najeriya, a wurin wani taron bikin cika shekaru 60 a duniya na tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilan ƙasar, Emeka Ihedioha.

Tsohon shugaban ya yi nuni da cewa idan aka kalli yadda tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln, ya bayyana tsarin dimokuradiyya da cewa gwamnati ce ta mutane da mutane ke jagoranta domin al’umma.

Inda ya ƙara da cewa tsari ne da ake domin kowa ya amfana, ba wai wani bangare na al’umma ba ko wasu mutane ƙalilan ba.

Obasanjo ya kuma bayyana cewa kafin zuwan dimokuradiyyar ƙasashen yamma, Afrika na da nata tsarin shugabancin wanda ke kula da buƙatun kowa.

A cewarsa wannan tsarin shi ne dimokuradiyya, ba abin da ake kira dimokuradiyya ba a yau wanda ke bai wa shugabanni damar karɓar duk abin da suke so ba bisa ƙa’ida ba da kuma ta hanyar cin hanci da rashawa su ce wa mutane su je kotu idan suna da ja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp