Home General Bani da alaƙa da masu fasa bututun Mai – Fubara

Bani da alaƙa da masu fasa bututun Mai – Fubara

Gwamnan jihar Rivers da aka dakatar, Siminalaya Fubara ya musanta zargin da ake yaɗawa cewa yana da alaƙa da ƙungiyoyin ƴanbindiga da ke fasa bututun mai, inda ya ce hotuna da bidiyo da ake yaɗawa ƙarya ne.

Fubara ya bayyana haka ne a wata sanarwa da sakataren watsa labaransa, Nelson Chukwudi ya fitar, inda ya ce Fubara na alla-wadai da yada labaran na farfaganda.

Ya ce ana yaɗa labaran na ƙaryar ne domin a tayar da zaune tsaye a jihar, sannan a ɓata masa suna,

“Gwamna Fubara ba shi da wata alaƙa da ƙungiyoyin ƴanbindiga masu fasa bututun mai, kuma bai taɓa tunanin ƙulla wata alaƙa da su ba, sannan kuma ba zai taɓa alaƙa da ɓatagari da suke barazana ga zaman lafiya da tattalin arzikin jihar Rivers ba,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Fubara ya nanata shirinsa na tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa, inda ya ƙara da cewa ba a cin moriyar gwamnati ba tare da zaman lafiya ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp