Home General Babu tabbacin Zan yi takara a 2027 -Atiku

Babu tabbacin Zan yi takara a 2027 -Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa babu tabbas ko zai tsaya takarar shugabancin ƙasar a zaɓen shekarar 2027.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da kafar talbijin ta Arise, wanda aka saki wani ɓangarenta a ranar Laraba.

An tambayi Atiku game da wanda zai jagoranci haɗakar da ƴan adawar ƙasar ke ƙoƙarin kafawa, sai Atiku ya ce tamkar abin da ya faru ne a lokacin da suka samar da jam’iyyar APC, inda bayan zaɓen fitar da gwani, dukkanin ƴan takarar suka mara wa mutum ɗaya baya, kuma ya yi nasara a babban zaɓen ƙasar.

Lokacin da aka tambaye shi ko zai yi takara, sai Atiku ya ce “ban sani ba, domin ya kamata ne a samar da kafa mai inganci tukuna.”

A makon da ya gabata ne Atiku Abubakar ya bayyana cewa ƴan adawa na ƙasar na tattaunawa domin yin haɗaka a ƙoƙarin tunkarar jam’iyya mai mulki a zaɓen Najeriya na 2027.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ne ya zo na biyu a zaɓen shugaban ƙasar na 2023, lokacin da Bola Tinubu ya samu nasara.

Sai dai tun bayan kama mulkin Tinubu al’ummar ƙasar na kokawa kan tashin farashin kayan masarufi da kuma tsadar rayuwa.

Masu lura da al’amuran yau da kullum a ƙasar na alaƙanta hakan da matakan da gwamnatin Tinubu ta ɗauka, kamar na cire tallafin man fetur da barin kasuwa ta tantance darajar kuɗin ƙasashen waje, abin da ya taimaka wajen karyewar darajar kuɗin kasar – naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp