Home General Alhaji Aminu Ado Bayero ya dakatar da hawan Karamar sallah a Kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya dakatar da hawan Karamar sallah a Kano

Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya dakatar da tsarin bikin hawan sallah karama.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran Sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya sanyawa hannu.

Ya ce bayan samun shawarwari da kiraye kiraye daga shugabanni da iyaye da Malamai da kuma tattaunawa da yan Majalisar Sarki ya zama wajibi a dakatar da hawan Sallah Karama na wannan shekara.

Sarkin ya ce Hawan Sallah ba abune na ko a mutu ko ayi rai ba, Wanda idan yin hakan zai kawo tashin hankali ko hargitsi da kawo rashin zaman lafiya to ya zama wajibi a hakura dayin hawan.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce a matsayinsa na Sarkin Kano ya dauki alkawarin kiyaye Imani da mutunci da dukiya da zaman lafiyar al’umma Wanda hakan ce ta sa ya ga dacewar daukar wannan mataki domin kaucewa dukkan wani abu daka iya kawo tashin hankali ko rashin samun zaman lafiya a tsakanin al’umma.

A don haka ne Mai Martaba Sarkin Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukaci al’umma da sauran masoya su yi hakuri da wannan hukunci da aka zartar domin samun dorewar zaman lafiya a jihar Kano da Kuma kasa baki daya.

Sarkin na Kano ya yi amfani da wannan dama wajan kira ga al’umma da su yi amfani da lokutan bukukuwan Sallah wajan ziyartar juna domin sada zumunci, inda ya taya al’umar musulmi murna da farin cikin gudanar da azumin watan Ramadan ya na mai addu’ar samu dacewar Ubangiji daga cikin bayinsa wadanda Allah yake gafartawa dayin rahama tareda karbar ibadar da aka gudanar

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp