Home General Nijeriya ta kama hanyar durkushewa- Peter Obi

Nijeriya ta kama hanyar durkushewa- Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi ya yi kira ga ƴan hamayya su riƙa magana kan abin da ya kira shugabanci maras kyau da ƙasar ke fuskanta, yayin da ya ce ta kama hanyar durƙushewa.

Yayin da yake jawabi a taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja ranar Laraba, Mista Obi ya koka kan yawan talaucin da halin matsi da ake fama da shi a ƙasar.

Ya ce abubuwa na ƙara lalacewa a ƙasar, kuma lokaci ya yi da za a haɗa kai wajen yin abin da ya dace, farawa daga jam’iyyarsa ta LP.

“Dole mu yi magana idan abubuwa suka lalace, Najeriya na kan hanyar durƙushewa, alƙaluma a bayyane suke, mutane da yawa na ƙara talaucewa, mutanen da a baya ke cin abinci mai kyau, yanzu sun koma mabarata…”.

“A baya idan na zo nan, mutane kan riƙa tambayata abin da nake son ci ko sha domin su kawo min, amma yanzu babu wanda yake tambayata, wannan na nuna halin talaucin da ƙasar nan ke ciki, don haka ya kamata mu tashi tsaye mu hada kai don yin gyara,” in ji Mista Obi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp