Home General Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Kungiyar Zago Akida ta jihar Kano ta kai ziyarar ga mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya Sanata Barau I Jibril Maliya.

Kungiyar karkashin jagorancin shugabanta Mukhtar BBA Gwammaja ta Kai ziyarar ne a gidan sanata dake birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Laraba bisa abin da ta kira managarta ayyukan da sanata yake yiwa Al’ummar jihar kano da kasa baki dai.

Da yake jawabi sanata Barau ya bayyana Jagoran kungiyar ta Zago Akida Marigayi Amb. Hon Alhaji Ahmadu Haruna Zago matsayin jajirtaccen ɗan siyasa bisa irin gudunmawar da ya bashi a fannin siyasar gidan sa.

Sanata Barau ya bayyana cewa “Nima dan Zago Akida ne, tabbas anyi babban rashi na Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago, amma Zago Akida ba marainiya nace, don zan zame mata gata wajen yi mata dukkan abin da take bukata.

Daga bisani sanata Barau ya Gwangwaje kungiya tlda kyautar kudi har Naira Miliyan 5 tare da bata kyautar mota gami da daukar alkawarin gami da daukar alkawarin samarwa da kungiyar dukkan abinda take bukata.

Da yake jawabi tun da bari shugaban kungiyar Mukhtar B.A Gwammaja ya godewa sanata Barau bisa karancin da ya nunawa ƙungiyar da kuma Marigayi Ambasada Ahmadu Haruna Zago.

Ya kuma bayyana cewa kungiyar zata cigaba da taimakawa kokarin sanatan ta ko wacce fuska.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp