Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirinta na gina tashoshin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai karfin megawatt 1,900 ga jihohin arewa 19, a wani bangare na ƙoƙarin bunkasa makamashin mara gurbata muhalli da kuma faɗaɗa cibiyoyin samar da lantarki ta ƙasa
Ministan Wutar Lantarkin Najeriya, Adebayo Adelabu, ne ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai karo na shida na 2025 da aka gudanar ranar Alhamis a Abuja, inda ya bayyana burin gwamnati na samar da kusan MW 8,000 na wutar lantarki kafin ƙarshen wa’adin mulkin Shugaba Bola Tinubu na farko a shekarar 2027.
Adelabu ya ce kowace tasha mai amfani da hasken rana za ta samar da kusan megawatt 100 na wutar lantarki, wanda hakan zai baiwa jihohi damar dogaro da kai da kuma rage dogaro da babbar cibiyar samar da wutar lantarki ta ƙasa.
Ya kuma bayyana cewa gwamnati na bin diddigin samun masu saka hannun jari masu zaman kansu don taimakawa wajen faɗaɗa babbar cibiyar lantarki ta ƙasa tare zamanantar da ita.
Read Also:
Wannan na zuwa ne daidai lokacin da ƴan Najeriya ke nuna damuwa dangane da yadda babbar cibiyar samar da lantarki ta ƙasa ke lalacewa tare da jefa ƙasa baki ɗaya cikin dubu a baya-bayan nan, musaman yankin arewa da ya fuskanci kalubale ta hanyar katsawar lantaki da aka alakanta da bata gari da ke lalata turakun wutan lantarki da kuma sata kayayyaki masu muhimmaci.
A watan Oktoban da ya gabata, barayin sun lalata muhimmin layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Kaduna mai karfin 330kV da ke samarwa jihohin Kano da Kaduna, da kuma wani layin da ke samar da Bauchi da Gombe da sauran sassan arewa maso gabas wuta.
Wannan lamari dai ya haifar da bacin rai na tsawon wata guda a jihohi 17 cikin 19 na arewacin ƙasar. Bayan gyare-gyaren, gwamnonin jihohin Arewa 19 sun yi kira da a samar da wutar lantarki masu zaman kansu ga jihohin domin tabbatar da ingantacciyar wutar lantarki a yankin.
Jihohin sun hada da Neja da Kwara da Kaduna da Kano da Jigawa daGombe da Katsina. Sauran sun hada da Sokoto da Zamfara da Bauchi da Yobe da Borno da Adamawa da Taraba da Naija da Filato da Nasarawa da Kogi da kuma Benue.
Sai dai da yake jawabi a wurin taron da kuma bayyana nasarorin da aka samu kawo yanzu, ministan ya jaddada cewa duba da hasken rana da Allah ya albarkaci Najeriya, babu dalilin da zai sa ƙasar ba za ta iya samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana ba.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 9 hours 8 minutes 44 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 10 hours 50 minutes 9 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com