Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa Maso Gabashin Najeriya

Ƙungiyar gwamnonin Arewa Maso Gabashin Najeriya ta ce za ta yi amfani dabaru daban-daban ta ƙarfi da lalama wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin bayanin bayan taro da gwamnan Taraba Agbu Kefas ya karanta bayan kammala taronsu karo na 11 a Damuturun jihar Yobe.

Gwamnonin sun ce dole ne a kawo ƙarshen matsalar rashin ayyukan yi na matasa, rashin ilimi mai inganci, rashin ababen more rayuwa da kuma sauran matsalolin da ke da alaƙa da talauci idan har ana son kawar da matsalar tsaro.

Yayin da zauren ke jinjinawa gwamnatin tarayyar ƙasar kan ƙoƙarinta a yaƙi da matsalar, ya kuma nuna damuwa game dawowar ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan yankin, a don haka su ka yi kira da jami’an tsaro da shugabannin al’umma su sake nazari kan dabarun yaƙi da matsalar.

Gwamnonin sun kuma nuna damuwa kan lalacewar manyan titunan ƙasar, wanda hakan ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

Ƙungiyar ta kuma ƙudiri aniyar ƙarfafa dangantakar mambobinta domin bunƙasa harkokin noma, makamashi, bayar da horo domin rage rashin aikin yi na matasa, da kuma tunkarar matsalolin sauyin yanayi.

Taron wanda gwamnan Borno kuma shugabansa Babagana Zulum ya jagoranta, ya samu halartar gwamnonin Adamawa, Borno, Gombe, Taraba da Yobe, yayin da na Bauchi mataimakinsa ya wakilce shi.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 7 hours 4 minutes 23 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 8 hours 45 minutes 48 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com