Hukumomi a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun tabbatar da tashin gobara a rumbun adana makamai da ke barikin sojoji da ake kira ‘Giwa Barrack’ a birnin Maiduguri.
Gobarar ta janyo fashewar abubuwa tare da haddasa fargaba a tsakanin al’umma a Maiduguri saboda ƙara mai ƙarfin gaske da aka ji a ƙwaryar birnin da kewaye.
Mazauna birnin Maiduguri sun shiga zulumi sakamakon tashin gobarar, inda galibin jama’a suka zaci cewa ‘yan Boko Haram ne suka kai hari.
Read Also:
Hukumar da ke kula da kashe gobara ta jihar Borno a cikin wata sanarwa, ta ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 10 da rabi na dare a ranar Laraba, inda ta lalata rumbun adana makamai na barikin sojojin.
Daga bisani ‘yan kwana-kwana sun samu nasarar kashe gobarar.
Binciken farko da hukumomi suka yi kan musababbin tashin gobarar, ya gano cewa tsananin zafi a Maiduguri na da alaƙa da tashin gobarar.
A shekara ta 2014 ne, ƙungiyar Boko Haram ta kai hari a barikin sojoji na Giwa lamarin da ya janyo hasarar rayuwa da dama.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 7 hours 24 minutes 2 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 9 hours 5 minutes 27 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com