Gwamnan Katsina ya ba da hutun aiki saboda ziyarar Tinubu

Gwamnan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ya ayyana yau Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin “tarɓar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu” da ke ziyara a jihar tasu.

Gwamna Dikko Radda ya bayyana hakan ne ranar Alhamis yayin jawabin da ya gabatar a taron Ranar Ma’aikata.

“Ina mai farin cikin shaida muku cewa Shugaba Tinubu zai kawo ziyara Katsina gobe [Juma’a] domin buɗe ayyuka da dama da muka kammala cikin shekara biyu da suka wuce,” in ji gwamnan.

“Saboda haka, na ayyana goben a matsayin ranar hutu saboda ma’aikata su samu damar haɗuwa da mu wajen tarɓar shugaban ƙasa.”

A jiya Alhamis ne fadar shugaban Najeriya ta sanar cewa Tinubu na jam’iyyar APC zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu a jihar da ke arewa maso yamma kuma ta tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1485 days 18 hours 55 minutes 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1467 days 20 hours 36 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com