Rahotanni daga ƙasar Kamaru sun ce barazanar kai harin mayakan Boko Haram a garin Garwa ya sanya hana Sallar Juma’ar da aka saba gudanarwa a yau, abin da ya jefa jama’a cikin ruɗani.
Read Also:
Bayanan sun ce tun da safe aka yi ta yaɗa labarin shirin kai harin ƴanta’addan, waɗanda suka zafafa hare-harensu a ƴan kwanakin nan, wannan ta sa shugabanni ɗaukar matakin dakatar da Sallar Juma’ar domin kare lafiyar jama’a.
Cikin manyan Masallatan da aka rufe yau har da Masallachin tsohon shugaban ƙasa Ahmadu Ahidjo.
Wakilin RFI hausa a Garwa Rilwanou Shehu Ousmane ya tabbatar da aukuwar lamarin.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 7 hours 41 minutes 54 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 9 hours 23 minutes 19 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com