Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta Najeriya, Jamb ta amince da saka sabuwar ranar sake jarrabawar UTME ga wasu ɗaliban da suka yi jarrabawar a wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar.
A wani taron manema labarai da shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede, ya gabatar a Abuja, babban binrin ƙasar ya ce hukumar ta amince da matsalolin da aka samu a jarrabawar UTME ta 2025,
Ya ƙara da cewa ɗalibai 206.610 ne za su sake jarrabawar a cibiyoyi 65 a Legas, yayin da a Owerri ɗalibai 173,387 za su sake jarrabawar a cibiyoyi 92.
Za a fara sake jarrabawar daga ranar 16 ga watan Mayu, inda za a aike da saƙon waya ga ɗaliban da lamarin ya shafa.
Read Also:
Shugaban hukumar ya kuma nemi afuwar ɗaliban kan matsaloli da aka fuskanta a lokacin jarrabawar.
“Na ɗauki alhakin duk abin da ya faru, kuma ina bayar da haƙuri ga ɗaliban da lamarin ya shafa”, in ji Farfesa Oyodele.
Farfesa Oloyode ya ce matsalar na’ura da aka samu a wasu santocin jihohin Legas da Owerri sun haifar da ƙorafe-ƙorafe daga wasu ɗaliban, inda hukumar ta gano matsalar bayar fitowar sakamakon jarrabawar.
“Matsalar ta samo asali ne daga ɗaya daga cikin kamfanonin da ke bai wa hukumarsu sadarwar, wanda jami’ansa suka kasa magance matsalar ta yadda hakan ya shafi wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar,” in ji shugaban hukumar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1485 days 18 hours 50 minutes 22 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1467 days 20 hours 31 minutes 47 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com