Shugaba Bola Tinubu ya ce Najeriya ta kama hanyar inganta kuma lokacin matsi ya wuce.
A jawabinsa na cika shekara biyu da karɓar ragamar mulki, Tinubu ya amince cewa tsare-tsarensa na kawo gyara sun janyo matsi kuma bai raina haƙuri da kuma uzurin da ƴan Najeriya suka nuna masa ba.
“A yau ina alfahari cewa sauye-sauyen mu a fannin tattalin arziki suna aiki. Mun kama hanyar samar da ƙasa mai ƙarfin tatalin arziki,” in ji shi.
A ranar da aka rantsar da shi a cikin watan Mayun 2023, shugaba Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur da aka daɗe ana cece ku-ce a kai, lamarin da ya janyo tsadar rayuwa a ƙasar.
Tinubu ya ce: “Duk da tsadar rayuwa da muka faɗa, mun samu ci gaba sosai. Hauhawar farashi ta fara raguwa musamman a kan farashin shinkafa da sauran kayayyaki.”
Alƙaluman da hukumomi suka fitar sun nuna cewa hauhawar farashi ya ƙaru zuwa kashi 24 cikin ɗari a watan da ya gabata, idan aka alaƙanta da kashi 22 da ake ciki a lokacin da Tinubu ya karɓi mulki.
A haka ma an samu raguwa ne idan aka kwatanta da kashi 34 da aka samu a shekarar da ta gabata, lamarin da ya janyo zanga-zanga a sassan ƙasar har ta kai ga asarar rayuka.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1461 days 22 hours 35 minutes 57 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 17 minutes 22 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com