Home General Rayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta – Tinubu

Rayuwar ƴan Najeriya na ƙara inganta – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya ce Najeriya ta kama hanyar inganta kuma lokacin matsi ya wuce.

A jawabinsa na cika shekara biyu da karɓar ragamar mulki, Tinubu ya amince cewa tsare-tsarensa na kawo gyara sun janyo matsi kuma bai raina haƙuri da kuma uzurin da ƴan Najeriya suka nuna masa ba.

“A yau ina alfahari cewa sauye-sauyen mu a fannin tattalin arziki suna aiki. Mun kama hanyar samar da ƙasa mai ƙarfin tatalin arziki,” in ji shi.

A ranar da aka rantsar da shi a cikin watan Mayun 2023, shugaba Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur da aka daɗe ana cece ku-ce a kai, lamarin da ya janyo tsadar rayuwa a ƙasar.

Tinubu ya ce: “Duk da tsadar rayuwa da muka faɗa, mun samu ci gaba sosai. Hauhawar farashi ta fara raguwa musamman a kan farashin shinkafa da sauran kayayyaki.”

Alƙaluman da hukumomi suka fitar sun nuna cewa hauhawar farashi ya ƙaru zuwa kashi 24 cikin ɗari a watan da ya gabata, idan aka alaƙanta da kashi 22 da ake ciki a lokacin da Tinubu ya karɓi mulki.

A haka ma an samu raguwa ne idan aka kwatanta da kashi 34 da aka samu a shekarar da ta gabata, lamarin da ya janyo zanga-zanga a sassan ƙasar har ta kai ga asarar rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp