Home General An kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano

An kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano

Rundunar ƴansanda a jihar Kano ta ce ta kama mutane 41 da ake zargi da hannu a kisan baturen ƴansanda na Rano, CSP Baba Ali.

Kwamishinan ƴansanda a jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ce kisan jami’in nasu babban abin takaici da tashin hankali ne.

Kisan jami’in ya janyo suka daga ɓangarori da dama, musamman a lokacin da bidiyon mummunan al’amarin ya riƙa yawo a shafukan sada zumunta.

A cikin sanarwar da rundunar, reshen jihar Kano ta fitar a yau Alhamis, kwamishinan ƴansandan ya ce rundunar tana yin duk abin da ya dace domin ganin an gurfanar da masu hannu a kisan jami’in nata da kuma tabbatar da cewa sun fuskanci hukunci daidai da abin da suka aikata.

Rundunar ta kuma buƙaci jama’a su ci gaba da gudanar da harkokin su na yau da kullum, yayin da jami’an rundunar ke ci gaba da aikin zaƙulo masu hannu a kisan da ma sauran laifuka domin su fuskanci hukunci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp