Home General Sojoji sun ce sun hallaka ƴan ta’adda 60 a jihar Borno

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojin Najeriya na Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan ta da ƙayar-baya sama da 60 a wani artabu da suka yi a jihar Borno.

Wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta fitar ranar Juma’a, ta ce dakarun sun samu nasarar kashe ƴan ta’ddan ne bayan bata-kashi da suka yi daddare a yankin Bita na jihar.

Sanarwar ta ce ƴan ta da ƙayar-bayan sun far wa sojojin birget 26 ne da misalin karfe 1:09 na asubahin yau Juma’a, inda dakarun Haɗin-Kai suka mayar da martani da hare-hare ta sama da kuma ƙasa kan ɓata-garin.

“Sojoji sun kaddamar da hare-haren sama da kuma ta ƙasa kan sansanonin ƴan ta da ƙayar baya a yankin Bita na jihar Borno da asubahin yau Juma’a, lamarin ya kai ga hallaka aƙalla 60 daga cikinsu,” a cewar sanarwar sojojin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp