Gwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke cika shekara biyu da soma wa’adin mulkinta na farko, hadaddiyar kungiyar kwadagon kasar ta NLC ta bayyana gwamnatin a matsayin wadda ta kasa cika alkawarrun da ta dauka a bangarori da dama.

Kungiyar ta NLC ta ce ikirarin shugaban kasar na cewa lokacin wahalar rayuwa ya zo karshe, na tamkar yaudara ce kasancewar manufofi da tsare-tsaren gwamnatin sun jefa fiye da ‘yan Najeriya miliyan 150 a cikin tsananin talauci da tsadar rayuwa.

A cikin wani bayani da ta fitar, Kungiyar kwadagon ta Najeriya ta bakin shugabanta Kwamared Joe Ajaero ya ce babu komi a cikin tafiyar wannan gwamnati face maimaita gazawar da gwamnatin da ta gada ta yi ne musamman a bangaren sabunta fata da manufofi.

To sai dai jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ta mayar da martini ga kungiyar ta kwadago ta NLC, inda ta ce babu adalci a maganar ‘yan kwadagon sannan ba su yi bincike mai zurfi ba, kafin furta wadannan kalamai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com