Home General Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Sojojin Najeriya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram da ISWAP

Nigerian Army

Rundunar sojojin Najeriya ta samu gagarumar nasarar kashe manyan manyan kwamandojin Boko Haram da na tsagin ISWAP, a wasu hare-hare da ta kai a makon da ya gabata da kuma wannan makon da mu ke ciki.

A wasu hare-hare da sojojin da ke aiki a ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai suka kai garuruwan Mallam Fatori da kuma Buratai na jihar Borno a makon da ya gabata, sun samu nasarar kashe kwamandojin Boko Haram uku da suka haɗa da Amir Abu Ali da Amir Ibunu sai kuma Amir Abu Waldume.

Haka nan a wani harin na daban da suka kai Nzalgana na jihar Yobe da kuma Timbuktu na jihar Borno, jami’an tsaron na Najeriya sun kashe Ameer Malam Jidda, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin Boko Haram a garin Ngorgore da Malumti.

Kisan manyan jagororin Boko Haram da sojojin Najeriya suka dai ya raunata tsarin shugabancinsu da kuma sanyasu cikin ɗimuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp