Home General Tinubu ya jajanta wa al’ummomin Kaduna da Kano da kuma Borno kan...

Tinubu ya jajanta wa al’ummomin Kaduna da Kano da kuma Borno kan mutuwar mutanensu

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu matafiya 12 a karamar hukumar Mangu ta jihar Filato a hanyarsu ta zuwa ɗaurin auren ɗan’uwansu.

Ya buƙaci jami’an tsaro su tabbatar da kama masu laifin tare ganin an hukunta su.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkokin yaɗa labaru Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, shugaban ya ce ba za su lamunci aikata irin haka ba.

“Kowane ɗan ƙasa na da ƴancin yin tafiya zuwa kowane ɓangare na ƙasar nan,” in ji Tinubu.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe da kuma gwamnatin jihar Kaduna, inda ya yi kira da a kwantar da hankali tare da alkawarin cewa sai an hukunta maharan.

A ɗaya gefen, Tinubu ya nuna kaɗuwa kan mutuwar wasu mutum 10 da ƴar ƙunar bakin wake ta hallaka a babbar kasuwar kifi da ke karamar hukumar Konduga na jihar Borno ranar Asabar.

Ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga gwamnati da kuma al’ummar jihar kan lamarin da ya faru.

“Na bai wa jami’an tsaro umarnin matsa ƙaimi don farauto ƴan Boko Haram da suka rage don daƙile ayyukansu. Na kuma bai wa hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA umarnin tallafawa waɗanda abin ya shafa,” in ji shugaban Najeriyar.

Har ila yau, ya sake miƙa ta’azziyarsa ga mutum biyar da suka mutu a wata fashewa a jihar Kano.

Ya buƙaci hukumomi su gudanar da bincike don gano abin da ya haddasa fashewar tare da ɗaukar matakan da suka dace don kare afkuwarsa a gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp