Home General Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zargin yin biris da ƴan ƙasarta dake Iran dai-dai lokacin da yaƙi ke ƙara rinchaɓewa a tsakanin Isra’ila da Iran ɗin.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Kimiebi Imomotimi Ebienfa ta ce zargin bashi da tsuhe ballantana makama.

A cewar sanarwar gwamnatin Najeriya, ƙarƙashin ma’aikatar harkokin waje na iya bakin ƙoƙarinta don tabbatar da cewa ƴan Najeriya mazauna Tehran na cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an baiwa ma’aikatan da ke yiwa gwamnatin Najeriya aiki a Iran damar aiki daga gida, sakamakon hare-haren da ke faɗawa sassan birnin.

Ma’aikatar harkokin wajen ta kuma ƙara da cewa tuni gwamnati ta fara aiki tare da gwamnatin Armenia don duba yadda ƴan Najeriya mazauna Iran ɗin zasu tsallaka ƙasar don samun mafaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp