Home General Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Bola Ahned Tinubu

Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zargin yin biris da ƴan ƙasarta dake Iran dai-dai lokacin da yaƙi ke ƙara rinchaɓewa a tsakanin Isra’ila da Iran ɗin.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Kimiebi Imomotimi Ebienfa ta ce zargin bashi da tsuhe ballantana makama.

A cewar sanarwar gwamnatin Najeriya, ƙarƙashin ma’aikatar harkokin waje na iya bakin ƙoƙarinta don tabbatar da cewa ƴan Najeriya mazauna Tehran na cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an baiwa ma’aikatan da ke yiwa gwamnatin Najeriya aiki a Iran damar aiki daga gida, sakamakon hare-haren da ke faɗawa sassan birnin.

Ma’aikatar harkokin wajen ta kuma ƙara da cewa tuni gwamnati ta fara aiki tare da gwamnatin Armenia don duba yadda ƴan Najeriya mazauna Iran ɗin zasu tsallaka ƙasar don samun mafaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp