Home General Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirin kwashe ƴan ƙasarta daga Iran

Bola Ahned Tinubu

Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zargin yin biris da ƴan ƙasarta dake Iran dai-dai lokacin da yaƙi ke ƙara rinchaɓewa a tsakanin Isra’ila da Iran ɗin.

A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Kimiebi Imomotimi Ebienfa ta ce zargin bashi da tsuhe ballantana makama.

A cewar sanarwar gwamnatin Najeriya, ƙarƙashin ma’aikatar harkokin waje na iya bakin ƙoƙarinta don tabbatar da cewa ƴan Najeriya mazauna Tehran na cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an baiwa ma’aikatan da ke yiwa gwamnatin Najeriya aiki a Iran damar aiki daga gida, sakamakon hare-haren da ke faɗawa sassan birnin.

Ma’aikatar harkokin wajen ta kuma ƙara da cewa tuni gwamnati ta fara aiki tare da gwamnatin Armenia don duba yadda ƴan Najeriya mazauna Iran ɗin zasu tsallaka ƙasar don samun mafaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp