Home General Waɗanda suka tsira daga kisan Filato sun bayyana yadda sojoji suka cece...

Waɗanda suka tsira daga kisan Filato sun bayyana yadda sojoji suka cece su

Wasu daga cikin waɗanda suka tsira daga kisan da aka yi wa wasu da za su je biki a Filato sun bayyana wa jaridar Daily Trust yadda aka kai musu hari a lokacin da suke tafiya zuwa bikin aure.

Ibrahim Umar, ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira, ya ce suna kan hanyarsu ne daga Zariya zuwa Qua’an Pan domin bikin ɗan uwansa. A cikin motar akwai mahaifin ango, kawunsa da kuma ƙaninsa. Duk da cewa sun bayyana wa maharan cewa ba ‘yan yankin ba ne, kuma suna ɗauke da goro da kyaututtukan biki, sai ya ce, “ba su saurare mu ba – suka kashe ƴanuwanmu.”

Ya bayyana cewa mahaifi da ƙanin ango da kuma kawunsa duk an kashe su a harin.

Angon, wanda asalinsa daga Zariya ne kuma malami ne a wata makaranta a yankin, ya hadu da matar da zai aura a lokacin da yake koyarwa, sannan suka amince su yi aure. Ibrahim ya ce sun bayyana wa maharan cewa ba mazauna yankin ba ne, daga Jihar Kaduna suka taho domin halartar biki, amma ba su yarda ba “Dukkanmu dangin juna ne, daga ƙauye ɗaya muka fito,” in ji shi.

Ibrahim ya ce da ba don sojojin da ke kusa da inda lamarin ya faru sun hanzarta zuwa ba, da abin zai fi muni. “Sojojin sun iso da wuri kuma suka cece mu. In ba don hakan ba, da labarin zai canza,” in ji shi.

Wani, wanda shi ma ya tsira daga harin, Sa’adu Abdullahi, ya bayyana cewa sun yi ɓatan hanya ne suka shiga wani ƙauye ba da gangan ba. Bayan sun tsaya domin tambayar hanya, sai kwatsam aka fara kai musu hari.

Duk da cewa sun shaida wa mutanen cewa suna kan hanyar zuwa biki ne, hakan bai sa aka kyale su ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp