Home Labarai Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da gano wasu bama-bamai 9 da ba su fashe ba.

Mataimakin kakakin rundunar na jihar Kano, DSP Hussaini Abdullahi, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar aka raba manema labarai a jihar, inda ya ce an gano bama-baman ne a gurin da bom ya fashe a kusa da wani kamfanin karafa na Yongxing Steel Company, da ke kan hanyar Ring Road ta unguwar Mariri.

A cewar sanarwar, “Bayan gano bama-bamai 7 da ba su fashe ba a baya, an sake bankado wasu guda biyu, wanda hakan ya kai adadin gaba ɗaya zuwa tara”.

Binciken ‘yan sanda ya gano cewa an haɗa bama-baman ne da shara, wadda aka kawo daga Jihar Yobe ba tare da an sani ba, kuma ɗaya daga cikinsu ya fashe yayin da ake sauke kayan a kamfanin.

don haka rundunar ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu kuma su ci gaba da sanar da hukumomin tsaro da zarar sun ga wani abu da ya daure musu kai wanda basu gamsu da shi ba.

A ƙarshe Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu guda biyar, tare da yi wa waɗanda ke jinya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp