Home Labarai Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da gano wasu bama-bamai 9 da ba su fashe ba.

Mataimakin kakakin rundunar na jihar Kano, DSP Hussaini Abdullahi, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar aka raba manema labarai a jihar, inda ya ce an gano bama-baman ne a gurin da bom ya fashe a kusa da wani kamfanin karafa na Yongxing Steel Company, da ke kan hanyar Ring Road ta unguwar Mariri.

A cewar sanarwar, “Bayan gano bama-bamai 7 da ba su fashe ba a baya, an sake bankado wasu guda biyu, wanda hakan ya kai adadin gaba ɗaya zuwa tara”.

Binciken ‘yan sanda ya gano cewa an haɗa bama-baman ne da shara, wadda aka kawo daga Jihar Yobe ba tare da an sani ba, kuma ɗaya daga cikinsu ya fashe yayin da ake sauke kayan a kamfanin.

don haka rundunar ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu kuma su ci gaba da sanar da hukumomin tsaro da zarar sun ga wani abu da ya daure musu kai wanda basu gamsu da shi ba.

A ƙarshe Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu guda biyar, tare da yi wa waɗanda ke jinya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp