Home Labarai Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da gano wasu bama-bamai 9 da ba su fashe ba.

Mataimakin kakakin rundunar na jihar Kano, DSP Hussaini Abdullahi, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar aka raba manema labarai a jihar, inda ya ce an gano bama-baman ne a gurin da bom ya fashe a kusa da wani kamfanin karafa na Yongxing Steel Company, da ke kan hanyar Ring Road ta unguwar Mariri.

A cewar sanarwar, “Bayan gano bama-bamai 7 da ba su fashe ba a baya, an sake bankado wasu guda biyu, wanda hakan ya kai adadin gaba ɗaya zuwa tara”.

Binciken ‘yan sanda ya gano cewa an haɗa bama-baman ne da shara, wadda aka kawo daga Jihar Yobe ba tare da an sani ba, kuma ɗaya daga cikinsu ya fashe yayin da ake sauke kayan a kamfanin.

don haka rundunar ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu kuma su ci gaba da sanar da hukumomin tsaro da zarar sun ga wani abu da ya daure musu kai wanda basu gamsu da shi ba.

A ƙarshe Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu guda biyar, tare da yi wa waɗanda ke jinya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp