Home Labarai Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘yansanda a Kano ta gano Bama-bamai 9

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta tabbatar da gano wasu bama-bamai 9 da ba su fashe ba.

Mataimakin kakakin rundunar na jihar Kano, DSP Hussaini Abdullahi, ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar aka raba manema labarai a jihar, inda ya ce an gano bama-baman ne a gurin da bom ya fashe a kusa da wani kamfanin karafa na Yongxing Steel Company, da ke kan hanyar Ring Road ta unguwar Mariri.

A cewar sanarwar, “Bayan gano bama-bamai 7 da ba su fashe ba a baya, an sake bankado wasu guda biyu, wanda hakan ya kai adadin gaba ɗaya zuwa tara”.

Binciken ‘yan sanda ya gano cewa an haɗa bama-baman ne da shara, wadda aka kawo daga Jihar Yobe ba tare da an sani ba, kuma ɗaya daga cikinsu ya fashe yayin da ake sauke kayan a kamfanin.

don haka rundunar ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu kuma su ci gaba da sanar da hukumomin tsaro da zarar sun ga wani abu da ya daure musu kai wanda basu gamsu da shi ba.

A ƙarshe Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya mika sakon ta’aziyyar sa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu guda biyar, tare da yi wa waɗanda ke jinya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp