Sakamakon mahawara mai zafi da kuma sukar da ta biyo bayan sabuwar dokar masarautun jihar Adamawa dake Najeriya, wadda aka ce ta tube rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar, gwamnan jihar Umaru Fintiri ya ce ba haka lamarin yake ba.
Read Also:
Fintiri wanda ya yi watsi da zargin cewar an yi dokar ce domin musgunawa wasu masu rike da sarautar gargajiya a jihar, cikin su harda tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya ce babu wani mai sarauta da aka sauke yanzu haka.
Gwamnan ya ce Lamidon Adamawa ne zai fayyace matsayin sarautar Atiku na Wazirin Adamawa da kuma makomarsa kamar yadda sabuwar dokar masarautun jihar ta tanada.
Fintiri ya ce Wazirin Adamawa sarauta ce kawai, amma baya daga cikin masu zaben Sarki ko kuma zama mukami na biyu bayan Lamidon Adamawa.
Gwamnan ya ce Masarautun jihar ce za su tantance masu zaben sarki da kuma ƴan majalisar sa daidai da sabuwar dokar da aka yi.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1470 days 22 hours 48 minutes 0 second,
Baptist School Students, Kaduna
1453 days 29 minutes 25 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com