Home Labarai Ranar 1 ga watan Janairun 2026 ne za a fara amfani sabbin...

Ranar 1 ga watan Janairun 2026 ne za a fara amfani sabbin dokokin haraji a Najeriya

Shugaban hukumar tara kuɗaɗen haraji ta Najeriya Zacch Adedeji, ya ce a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2026 ne sabbin dokokin tattara harajin da shugaban ƙasar ya sanyawa hannu a jiya ne za su fara aiki.

Ya ce tazarar watanni shidan da aka samu, zai baiwa gwamnati damar shiryawa da wayar da kan al’umma da kuma daidaita kasafin kuɗin ƙasar.

Bisa la’akari da yadda ake gudanar da al’amura, idan aka samu irin wannan sauyi, yana ɗaukar lokaci kafin duk masu ruwa da tsaki a ɓangaren su sauya tsarin da ake amfani da shi.

Adedeji ya jaddada mahimmancin fara amfani da sauye-sauyen a farkon shekara, yana mai cewar hakan zai baiwa masu ruwa da tsaki damar aiwatar da shi yadda ya kamata saɓanin a tsakiyar shekara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp