Shugaban hukumar tara kuɗaɗen haraji ta Najeriya Zacch Adedeji, ya ce a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2026 ne sabbin dokokin tattara harajin da shugaban ƙasar ya sanyawa hannu a jiya ne za su fara aiki.
Read Also:
Adedeji ya dai bayyana hakan ne a lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi a jiya Alhamis, jim kaɗan bayan sanya hannu don sabuwar dokar haraji da shugaba Tinubu ya yi.
Ya ce tazarar watanni shidan da aka samu, zai baiwa gwamnati damar shiryawa da wayar da kan al’umma da kuma daidaita kasafin kuɗin ƙasar.
Bisa la’akari da yadda ake gudanar da al’amura, idan aka samu irin wannan sauyi, yana ɗaukar lokaci kafin duk masu ruwa da tsaki a ɓangaren su sauya tsarin da ake amfani da shi.
Adedeji ya jaddada mahimmancin fara amfani da sauye-sauyen a farkon shekara, yana mai cewar hakan zai baiwa masu ruwa da tsaki damar aiwatar da shi yadda ya kamata saɓanin a tsakiyar shekara.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1471 days 9 hours 37 minutes 14 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1453 days 11 hours 18 minutes 39 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com