Home Labarai NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Wani harin sojin saman Nijeriya ya yi sanadiyyar mutuwar ayarin ‘Yantadda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Rundunar Sojin saman Nijeriya karkashin dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sami nasarar tarwatsa ayarin ‘yanta’adda dake kan hanyar Kebbi zuwa Zamfara a Arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labara da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya Air Commodore Edward Gabkwet ya aikewa PRNigeria a ranar laraba.

Ya ce bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi na cewa ‘yan ta’addan na kokarin yin wani ayari na akalla Babura 150 ko wane dauke da bindigu guda 2 a kusa da kauyen Yarbuga dake karamar hukumar Maru a jihar zamfara domin gudanar da ayyukan ta’addanci a yankin.

Bayan tabbatar da rahoton dakarun rundunar suka gudanar da hari kan ayarin ‘yan bindiga, wanda ya yi sanadiyar hallaka da dama tare da raunata wasu, wadanda suka gudu cikin daji da raunika harbi a jukkunansu, tare da barin tarin makama da baburan hawa, rahotannin daga rundunar na bayyana cewa yanzu haka dakarun rundunar sun tare dukkannin hanyoyi domin hana musu guduwa.

Haka kuma rana 10 ga watan Yuni dakarun sun fantsama cikin kauyen na Yarbuga inda suka sake yin wata arangama, wanna ya basu nasarar gano sauran ‘yanta’addan da suka gudu da runuka a jikin su tare da kone baburansu da kuma kwato makamai.

Gabkwet ya bayyana cewa wannan hari na daga cikin kokarin da dakarun suke na tabbatar da kawo karshen tashin hankalin dake faruwa a yankin Arewa Maso yammacin Nijeriya tare da tabbatar da tsaron rayukan Al’ummar.

Daga  PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp