Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram 24

Sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram 24

Nigerian Army

Sojojin Najeriya – ƙarƙashin rundunar ‘Operation Hadin Kai’ mai yaƙi da ta’addanci – sun kashe mayaƙan Boko Haram 24 a wani mummunan hari da suka ƙaddamar kan maɓoyarsu a yankin raewa maso gabashin Najeriya.

Mataimakin dakartan hulda da jama’a na rundunar, Captain Reuben Kovangiya ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

Captain Kovangiya ya ce cikin wadanda aka kashe har da mutum biyar da ke samar wa mayaƙan makamai, waɗanda aka yi wa kwanton-ɓauna a wani samame da sojojin suka ƙadamar cikin dare.

Sanarwar ta ce sojojin sun ƙaddamar hare-haren ne dajin Sambisa da yankin Timbuktu da tsaunukan Mandara da wasu wurare, tun daga ranar 4 zuwa 9 ga watan da muke ciki.

Sojojin sun kuma samu nasarar ƙwato makamai da alburusai da wasu kayyakin yaƙin ƙungiyar ta Boko Haram.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp