Home Labarai NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Wani harin sojin saman Nijeriya ya yi sanadiyyar mutuwar ayarin ‘Yantadda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Rundunar Sojin saman Nijeriya karkashin dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sami nasarar tarwatsa ayarin ‘yanta’adda dake kan hanyar Kebbi zuwa Zamfara a Arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labara da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya Air Commodore Edward Gabkwet ya aikewa PRNigeria a ranar laraba.

Ya ce bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi na cewa ‘yan ta’addan na kokarin yin wani ayari na akalla Babura 150 ko wane dauke da bindigu guda 2 a kusa da kauyen Yarbuga dake karamar hukumar Maru a jihar zamfara domin gudanar da ayyukan ta’addanci a yankin.

Bayan tabbatar da rahoton dakarun rundunar suka gudanar da hari kan ayarin ‘yan bindiga, wanda ya yi sanadiyar hallaka da dama tare da raunata wasu, wadanda suka gudu cikin daji da raunika harbi a jukkunansu, tare da barin tarin makama da baburan hawa, rahotannin daga rundunar na bayyana cewa yanzu haka dakarun rundunar sun tare dukkannin hanyoyi domin hana musu guduwa.

Haka kuma rana 10 ga watan Yuni dakarun sun fantsama cikin kauyen na Yarbuga inda suka sake yin wata arangama, wanna ya basu nasarar gano sauran ‘yanta’addan da suka gudu da runuka a jikin su tare da kone baburansu da kuma kwato makamai.

Gabkwet ya bayyana cewa wannan hari na daga cikin kokarin da dakarun suke na tabbatar da kawo karshen tashin hankalin dake faruwa a yankin Arewa Maso yammacin Nijeriya tare da tabbatar da tsaron rayukan Al’ummar.

Daga  PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp