Home Labarai NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Wani harin sojin saman Nijeriya ya yi sanadiyyar mutuwar ayarin ‘Yantadda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Rundunar Sojin saman Nijeriya karkashin dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sami nasarar tarwatsa ayarin ‘yanta’adda dake kan hanyar Kebbi zuwa Zamfara a Arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labara da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya Air Commodore Edward Gabkwet ya aikewa PRNigeria a ranar laraba.

Ya ce bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi na cewa ‘yan ta’addan na kokarin yin wani ayari na akalla Babura 150 ko wane dauke da bindigu guda 2 a kusa da kauyen Yarbuga dake karamar hukumar Maru a jihar zamfara domin gudanar da ayyukan ta’addanci a yankin.

Bayan tabbatar da rahoton dakarun rundunar suka gudanar da hari kan ayarin ‘yan bindiga, wanda ya yi sanadiyar hallaka da dama tare da raunata wasu, wadanda suka gudu cikin daji da raunika harbi a jukkunansu, tare da barin tarin makama da baburan hawa, rahotannin daga rundunar na bayyana cewa yanzu haka dakarun rundunar sun tare dukkannin hanyoyi domin hana musu guduwa.

Haka kuma rana 10 ga watan Yuni dakarun sun fantsama cikin kauyen na Yarbuga inda suka sake yin wata arangama, wanna ya basu nasarar gano sauran ‘yanta’addan da suka gudu da runuka a jikin su tare da kone baburansu da kuma kwato makamai.

Gabkwet ya bayyana cewa wannan hari na daga cikin kokarin da dakarun suke na tabbatar da kawo karshen tashin hankalin dake faruwa a yankin Arewa Maso yammacin Nijeriya tare da tabbatar da tsaron rayukan Al’ummar.

Daga  PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp