Home Labarai NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

NAF ta tarwatsa ayarin ‘Yanta’adda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Wani harin sojin saman Nijeriya ya yi sanadiyyar mutuwar ayarin ‘Yantadda a hanyar Kebbi zuwa Zamfara

Rundunar Sojin saman Nijeriya karkashin dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sami nasarar tarwatsa ayarin ‘yanta’adda dake kan hanyar Kebbi zuwa Zamfara a Arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labara da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya Air Commodore Edward Gabkwet ya aikewa PRNigeria a ranar laraba.

Ya ce bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi na cewa ‘yan ta’addan na kokarin yin wani ayari na akalla Babura 150 ko wane dauke da bindigu guda 2 a kusa da kauyen Yarbuga dake karamar hukumar Maru a jihar zamfara domin gudanar da ayyukan ta’addanci a yankin.

Bayan tabbatar da rahoton dakarun rundunar suka gudanar da hari kan ayarin ‘yan bindiga, wanda ya yi sanadiyar hallaka da dama tare da raunata wasu, wadanda suka gudu cikin daji da raunika harbi a jukkunansu, tare da barin tarin makama da baburan hawa, rahotannin daga rundunar na bayyana cewa yanzu haka dakarun rundunar sun tare dukkannin hanyoyi domin hana musu guduwa.

Haka kuma rana 10 ga watan Yuni dakarun sun fantsama cikin kauyen na Yarbuga inda suka sake yin wata arangama, wanna ya basu nasarar gano sauran ‘yanta’addan da suka gudu da runuka a jikin su tare da kone baburansu da kuma kwato makamai.

Gabkwet ya bayyana cewa wannan hari na daga cikin kokarin da dakarun suke na tabbatar da kawo karshen tashin hankalin dake faruwa a yankin Arewa Maso yammacin Nijeriya tare da tabbatar da tsaron rayukan Al’ummar.

Daga  PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp