Home Labarai Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar...

Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar Filato

‘Yan bindiga sun kai wani sabon hari a ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato, tare da kashe aƙalla manoma 27, a wani yanayi da hare-hare ke ci gaba da zafafa a jihar ta Arewacin Najeriya.

sun bayyana cewa tuni aka garzaya da mutanen da suka tsira da raunuka zuwa asibitin koyarwa na garin Jos da kuma sauran wasu asibitocin a cikin jihar.

Dalyop Solomon, shugaban ƙungiyar matasan Birom ta BYM ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, a cewarsa maharan sun kutsa yankin ne wurin ƙarfe 5:30 na Asuba a ranar Litinin, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi tare da cinnawa gidaje wuta.

Shugaban ya tabbatar da mutuwar mutane 27, inda ya ce za’a sanar da lokacin jana’izarsu nan gaba, yayin da da dama suka jikkata kuma aka garzaya dasu asibiti.

Tuni ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta barranta kanta daga harin.

Shugaban ƙungiyar na Filato, Ibrahim Babayo ya ce ko kusa basu da hannu a kai harin, yana mai cewa zarginsu da ake bashi da tushe ballantana makama.

Har zuwa wannan lokaci dai gwamnati ba ta ce komai kan harin ba, a wani yanayi da jihar ta tsakiyar arewacin Najeriya ke ci gaba da fama da rikice-rikice da ke haddasa asarar ɗimbin rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp