Home General Tarihi bazai manta da Buhari ba – Osibanjo

Tarihi bazai manta da Buhari ba – Osibanjo

President-Muhammadu-Buhari

Mataimakin shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya miƙa ta’aziyyarsa bisa rasuwar tsohon maigidansa, Muhammadu Buhari.

Osinbajo ya kasance abokin takarar Buhari a zaɓukan shugaban ƙasa na 2015 da 2019, kuma ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban kasa tare da Buhari na shekara takwas.

A saƙon ta’aziyyar da ya aike, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya wallafa cewa : ”Ni da mai dakina Dolapo mun sami labarin rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da rana”

Ya kuma ce ya yi magana da Aisha Buhari, matar tsohon shugaban ƙasar, da kuma ɗansa Yusuf Buhari domin miƙa ta’aziyyarsa da kuma taya su alhinin rashinsa, wanda a cewarsa yana alfahari da aiki tare da shi na tsawon shekara 8 da ba zai taɓa mantawa dasu ba.

Mista Osinbajo ya ce Najeriya ta yi asarar mai ƙishin ƙasa na asali, wanda rayuwarsa ta kasance cike da ayyukan da ke nuna sadaukarwa ga ƙasarsa da yake ƙauna.

” Tarihin Buhari zai bayar da shaida game da martaba aikin gwamnati da ke cike da gaskiya, da kuma sadaukarwa ga cigaban alumma,” in ji tsohon mataimakin shugaban ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp