Home General Tarihi bazai manta da Buhari ba – Osibanjo

Tarihi bazai manta da Buhari ba – Osibanjo

President-Muhammadu-Buhari

Mataimakin shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya miƙa ta’aziyyarsa bisa rasuwar tsohon maigidansa, Muhammadu Buhari.

Osinbajo ya kasance abokin takarar Buhari a zaɓukan shugaban ƙasa na 2015 da 2019, kuma ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban kasa tare da Buhari na shekara takwas.

A saƙon ta’aziyyar da ya aike, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya wallafa cewa : ”Ni da mai dakina Dolapo mun sami labarin rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da rana”

Ya kuma ce ya yi magana da Aisha Buhari, matar tsohon shugaban ƙasar, da kuma ɗansa Yusuf Buhari domin miƙa ta’aziyyarsa da kuma taya su alhinin rashinsa, wanda a cewarsa yana alfahari da aiki tare da shi na tsawon shekara 8 da ba zai taɓa mantawa dasu ba.

Mista Osinbajo ya ce Najeriya ta yi asarar mai ƙishin ƙasa na asali, wanda rayuwarsa ta kasance cike da ayyukan da ke nuna sadaukarwa ga ƙasarsa da yake ƙauna.

” Tarihin Buhari zai bayar da shaida game da martaba aikin gwamnati da ke cike da gaskiya, da kuma sadaukarwa ga cigaban alumma,” in ji tsohon mataimakin shugaban ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp