Home Labarai Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar...

Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar Filato

‘Yan bindiga sun kai wani sabon hari a ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato, tare da kashe aƙalla manoma 27, a wani yanayi da hare-hare ke ci gaba da zafafa a jihar ta Arewacin Najeriya.

sun bayyana cewa tuni aka garzaya da mutanen da suka tsira da raunuka zuwa asibitin koyarwa na garin Jos da kuma sauran wasu asibitocin a cikin jihar.

Dalyop Solomon, shugaban ƙungiyar matasan Birom ta BYM ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, a cewarsa maharan sun kutsa yankin ne wurin ƙarfe 5:30 na Asuba a ranar Litinin, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi tare da cinnawa gidaje wuta.

Shugaban ya tabbatar da mutuwar mutane 27, inda ya ce za’a sanar da lokacin jana’izarsu nan gaba, yayin da da dama suka jikkata kuma aka garzaya dasu asibiti.

Tuni ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta barranta kanta daga harin.

Shugaban ƙungiyar na Filato, Ibrahim Babayo ya ce ko kusa basu da hannu a kai harin, yana mai cewa zarginsu da ake bashi da tushe ballantana makama.

Har zuwa wannan lokaci dai gwamnati ba ta ce komai kan harin ba, a wani yanayi da jihar ta tsakiyar arewacin Najeriya ke ci gaba da fama da rikice-rikice da ke haddasa asarar ɗimbin rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp