Home Labarai Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar...

Ƴanbindiga sun sake kashe manoma 27 a harin da suka kai jihar Filato

‘Yan bindiga sun kai wani sabon hari a ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato, tare da kashe aƙalla manoma 27, a wani yanayi da hare-hare ke ci gaba da zafafa a jihar ta Arewacin Najeriya.

sun bayyana cewa tuni aka garzaya da mutanen da suka tsira da raunuka zuwa asibitin koyarwa na garin Jos da kuma sauran wasu asibitocin a cikin jihar.

Dalyop Solomon, shugaban ƙungiyar matasan Birom ta BYM ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, a cewarsa maharan sun kutsa yankin ne wurin ƙarfe 5:30 na Asuba a ranar Litinin, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi tare da cinnawa gidaje wuta.

Shugaban ya tabbatar da mutuwar mutane 27, inda ya ce za’a sanar da lokacin jana’izarsu nan gaba, yayin da da dama suka jikkata kuma aka garzaya dasu asibiti.

Tuni ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta barranta kanta daga harin.

Shugaban ƙungiyar na Filato, Ibrahim Babayo ya ce ko kusa basu da hannu a kai harin, yana mai cewa zarginsu da ake bashi da tushe ballantana makama.

Har zuwa wannan lokaci dai gwamnati ba ta ce komai kan harin ba, a wani yanayi da jihar ta tsakiyar arewacin Najeriya ke ci gaba da fama da rikice-rikice da ke haddasa asarar ɗimbin rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp