Home Labarai Buhari mutum ne mai gaskiya da kishin ƙasa – IBB

Buhari mutum ne mai gaskiya da kishin ƙasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya Janar Ibrahim Babangida ya miƙa ta’aziyarsa bisa rasuwar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari inda ya bayyana shi da mutum mai kyawawan halaye, kuma mai kishin ƙasa.

IBB wanda ya hamɓarar da Buhari daga mulkin soji a ranar 27 ga watan Agustan 1985, ya bayyana shi a matsayin mutumin da ko bayan barinsa mulki, ya cigaba da kasance abin koyi ga mutane da dama kuma abin misali.

Ya kuma tuna lokacin da ya fara haɗuwa da marigayi Buhari a shekarar 1962 a lokacin da suka shiga makarantar horar da sojoji da ke Kaduna.

“Tun a lokacin Muhammadu Buhari mutum ne na daban, bai cika magana ba, amma yana da jajircewa, kuma mutum ne mai bin ƙa’ida kuma mai sauƙin kai, mai tsananin kishin ƙasa ne da sadaukar da kai ga Najeriya. A cikin shekarun, mun kasance tare cikin wahala da daɗi da jarabawa da kuma cin nasara da rashinsa.”

Babangida ya ce duk da shi da Buhari sukan saɓa kan wasu abubuwa, kamar yadda a kan samu tsakanin ƴanuwa, “amma ko kaɗan ban taɓa kokwanto game da gaskiyarsa da kishin ƙasa ba.

”Bayan aiki kuma na san shi a matsayin mutum mai addini wanda kuma ke tafiyar da rayuwarsa cikin tawali’u.” in ji tsohon shugaban mulkin sojin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp