Home Labarai Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami’an tsaro a Nigeria sun kama Mai Wasan barkwancinan a shafukan sada zumunta Dr. Bello Habib Galadanci wanda aka fi Sani da Danbello.

Danbello dai ya jima ya yin wasanni barkwanci inda a ciki yake nuna yadda Shugabanni a Nijeriya suka Gaza yiwa talakawan Kasar abubuwan da suka dace.

An dai kama Danbello ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Kano , Jim kadan bayan saukarsa daga jirgin sama .

Dama dai Danbello yana zaune ne a Kasar China inda daga chan yake yin duk abun da yake yi .

Ana zargin Jami’an tsaron da suka kama Danbellon sun zo ne daga Abuja.

Sai dai duk da cewa ba a bayyana dililin kama Danbello ba, Amma mintoci kadan bayan kama shin kuma aka sake shi .

A wata hirarsa da manema labarai Danbello ya ce ” Bayan sakkowarmu daga jirgi sai wasu mutane masu kama da Jami’an tsaro suka karbi Fasfo dina da sauran takarduna , kuma suka ce In shiga wata mota”.

” Ana haka sai ga Barr. Abba Hakima nan sai akai Dan yi waya sannan akai dogon turanci bayan awa daya sai suka sallameni, Amma dama ban yi mamakin kamani ba, don dama da Shirin hakan na zo.

Tuni dai Danbello yana cikin Iyalansa bayan sakinsa da Jami’an tsaron suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp