Home Labarai Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Yadda Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami’an tsaro a Nigeria sun kama Mai Wasan barkwancinan a shafukan sada zumunta Dr. Bello Habib Galadanci wanda aka fi Sani da Danbello.

Danbello dai ya jima ya yin wasanni barkwanci inda a ciki yake nuna yadda Shugabanni a Nijeriya suka Gaza yiwa talakawan Kasar abubuwan da suka dace.

An dai kama Danbello ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano dake Kano , Jim kadan bayan saukarsa daga jirgin sama .

Dama dai Danbello yana zaune ne a Kasar China inda daga chan yake yin duk abun da yake yi .

Ana zargin Jami’an tsaron da suka kama Danbellon sun zo ne daga Abuja.

Sai dai duk da cewa ba a bayyana dililin kama Danbello ba, Amma mintoci kadan bayan kama shin kuma aka sake shi .

A wata hirarsa da manema labarai Danbello ya ce ” Bayan sakkowarmu daga jirgi sai wasu mutane masu kama da Jami’an tsaro suka karbi Fasfo dina da sauran takarduna , kuma suka ce In shiga wata mota”.

” Ana haka sai ga Barr. Abba Hakima nan sai akai Dan yi waya sannan akai dogon turanci bayan awa daya sai suka sallameni, Amma dama ban yi mamakin kamani ba, don dama da Shirin hakan na zo.

Tuni dai Danbello yana cikin Iyalansa bayan sakinsa da Jami’an tsaron suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp