Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a Tafkin Chadi MNJTF ta ce ta yi nasarar kashe kwamandan ƙungiyar da mayaƙansa biyar.
Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Laraba ta ce dakarunta sun fafata da mayaƙan ne a yankin Koulfoua bayan kai musu hari, inda suka kashe kwamandan mai suna Amir Dumkei da wasu ‘yanbindiga biyar.
Read Also:
“‘Yanta’addan ne suka fara kawo hari da farar safiyar Talata a sansanin sojan MNJTF da ke Koulfoua, amma kuma sai suka hadu da ruwan wutar da ya fi ƙarfinsu,” a cewar sanarwar da Kanal Olaniyi Osoba ya fitar.
Ta ƙara da cewa ta ƙwace makamai da dama a hannunsu da suka haɗa da bindiga ƙirar AK-47 tara, da ƙananan jiragen ruwa uku, da ƙunshin harsasai mai girma.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1491 days 5 hours 12 minutes 43 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1473 days 6 hours 54 minutes 8 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com