Dakarun MNJTF sun kashe kwamandan Boko Haram a Tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a Tafkin Chadi MNJTF ta ce ta yi nasarar kashe kwamandan ƙungiyar da mayaƙansa biyar.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Laraba ta ce dakarunta sun fafata da mayaƙan ne a yankin Koulfoua bayan kai musu hari, inda suka kashe kwamandan mai suna Amir Dumkei da wasu ‘yanbindiga biyar.

“‘Yanta’addan ne suka fara kawo hari da farar safiyar Talata a sansanin sojan MNJTF da ke Koulfoua, amma kuma sai suka hadu da ruwan wutar da ya fi ƙarfinsu,” a cewar sanarwar da Kanal Olaniyi Osoba ya fitar.

Ta ƙara da cewa ta ƙwace makamai da dama a hannunsu da suka haɗa da bindiga ƙirar AK-47 tara, da ƙananan jiragen ruwa uku, da ƙunshin harsasai mai girma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com