Home Labarai KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata...

KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata titunan birnin Kano

Hukumar kula da zirga-zirga ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta kama direban wata motar gida saboda zarginsa da karya dokar tuki.

Hukumar ta KAROTA ta kama direban ne akan titin Murtala Muhammad dake birnin Kano bayan ya tsallaka titin ta wajen da bai dace ba, tare da taka fulawar titi da gwamnatin Kano ta kawata titin da su.

A wata ganawarsa da manema labarai mai magana da yawun hukumar ta KAROTA Malam Abubakar Ibrahim Sharada yace direban ya karya dokar hanya kuma za’a gabatar dashi a gaban kotu domin zama izinina ga masu kokarin karya dokar tuƙi a jihar.

Daga bisani Yaja kunne direbobi da su guji karya dokar hanya, yana mai cewa hukumar ta KAROTA ba zata zura idanu ba.

An zargin Direban da yiwa Jami’an hukumar gadara.

Tunda farko mai baiwa gwamnan Kano shawara kan harkokin yada Labarai Hon Ibrahim Adam shine ya wallafa yadda diraban ya karya dokar tukin, kuma hakan yaja hankalin hukumomin da abin ya shafa aka kamo diraban.

Ko dai a watan da ya gabata sai da gwamnatin Kano ta gurfanar da wasu masu awakai a gaban kotu saboda lalata cikawar da suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp