Home Labarai KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata...

KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata titunan birnin Kano

Hukumar kula da zirga-zirga ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta kama direban wata motar gida saboda zarginsa da karya dokar tuki.

Hukumar ta KAROTA ta kama direban ne akan titin Murtala Muhammad dake birnin Kano bayan ya tsallaka titin ta wajen da bai dace ba, tare da taka fulawar titi da gwamnatin Kano ta kawata titin da su.

A wata ganawarsa da manema labarai mai magana da yawun hukumar ta KAROTA Malam Abubakar Ibrahim Sharada yace direban ya karya dokar hanya kuma za’a gabatar dashi a gaban kotu domin zama izinina ga masu kokarin karya dokar tuƙi a jihar.

Daga bisani Yaja kunne direbobi da su guji karya dokar hanya, yana mai cewa hukumar ta KAROTA ba zata zura idanu ba.

An zargin Direban da yiwa Jami’an hukumar gadara.

Tunda farko mai baiwa gwamnan Kano shawara kan harkokin yada Labarai Hon Ibrahim Adam shine ya wallafa yadda diraban ya karya dokar tukin, kuma hakan yaja hankalin hukumomin da abin ya shafa aka kamo diraban.

Ko dai a watan da ya gabata sai da gwamnatin Kano ta gurfanar da wasu masu awakai a gaban kotu saboda lalata cikawar da suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp