Home Labarai KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata...

KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata titunan birnin Kano

Hukumar kula da zirga-zirga ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta kama direban wata motar gida saboda zarginsa da karya dokar tuki.

Hukumar ta KAROTA ta kama direban ne akan titin Murtala Muhammad dake birnin Kano bayan ya tsallaka titin ta wajen da bai dace ba, tare da taka fulawar titi da gwamnatin Kano ta kawata titin da su.

A wata ganawarsa da manema labarai mai magana da yawun hukumar ta KAROTA Malam Abubakar Ibrahim Sharada yace direban ya karya dokar hanya kuma za’a gabatar dashi a gaban kotu domin zama izinina ga masu kokarin karya dokar tuƙi a jihar.

Daga bisani Yaja kunne direbobi da su guji karya dokar hanya, yana mai cewa hukumar ta KAROTA ba zata zura idanu ba.

An zargin Direban da yiwa Jami’an hukumar gadara.

Tunda farko mai baiwa gwamnan Kano shawara kan harkokin yada Labarai Hon Ibrahim Adam shine ya wallafa yadda diraban ya karya dokar tukin, kuma hakan yaja hankalin hukumomin da abin ya shafa aka kamo diraban.

Ko dai a watan da ya gabata sai da gwamnatin Kano ta gurfanar da wasu masu awakai a gaban kotu saboda lalata cikawar da suka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp